Bitar labaran makon da ya gabata ta cikin shirin "Mu zagaya Duniya"
Manage episode 422555562 series 1237821
Shirin Mu zagaya duniya bisa al'ada kan yi bitar muhimman labaran da suka gudana a makon jiya, a wannan makon shirin tare da Nasrudden Muhammad, ya duba kan dambarwar yajin aikin NLC a Najeriya sai kuma yadda Jam'iyyar ANC a Afrika ta kudu ke laluben kafa gwamnatin haɗaka.
Duk dai a cikin shirin za kuma kuji yadda ta ke ci gaba da kayawa a Gaza, bayan da Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare sassan Rafah ciki har da makarantar da ke ƙarƙashin kulawar Majalisar Ɗinkin Duniya.
Waɗannan da ma sauran muhimman labarai na ƙunshe a cikin shirin.
Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin..
24 episoder